Thursday, 14 July 2016

  ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ”…53and54๐Ÿ”…

Kaya afham yashiga hadawa, saida yacika akwatinsa kaf, sannan ya tsaya yana tunanin idan yafita ina zai dosa, ina zaije,
  Kofar dakinsa yaji anturo, yakurawa kofar ido yana jiran yaga wazai shigo,
  Aneesah ce tayi tsaye tana kallon yana yinsa, akwatin data gani a gefensa ta kurawa ido cike mamaki tace "yaya afham mekake shirin aikatawa ne, naga kahada kaya"

  Afham yakauda kai daga kallon datake masa yaci gaba da rufe zip din akwatinsa, saida ya kammala rufewa yadaga kai yasake kallon aneesah "gidan nan zan bari, kuma idan natafi kigayawa su abba karsu nemeni, domin nabar gidan nan har abada, domin nayi shawara da zuciyata barin gidan nan shine kadai katangata agareni akan auren amal "

  Mamaki yacika aneesah sosai, tarike kugu tana kallon afham "hmm yaya afham zuciyarka bata baka shawarar kwaraiba, domin tanema maka saukankiyar hanya wadda zata saka mahalincinka (Allah) Fushi dakai, domin yardar Allah tana tare da yardar iyaye, fushin Allah yana tare da fushin iyaye, yaya afham kayi gaggawar chanza wannan gurguwar shawarar taka, mezaka cewa Allah yanzu idan katafi kaddara takiraka kasamu matsala atafiyarka, zakacene kayi fushi da iyayenka shine kabar musu gida, mafi aka sarin irin wannan tafiyar bata zama alkhairi, yaya afham karkaje, kazauna cikin ahalinka shine mafi alkhairi agareka "

  edon afham yayi jajir cike da masifa yace "yakikeson nayi kenan natsaya a auramun wacca bana so, nifa kwata2 bana son amal, wlh matukar ba'a rabani da amal ba to wallahi zanbar gidan nan"

  Aneesah tayi ajiyar zuciyar, tana mamakin irin zuciyar afham shi baya daukar nasiha, a duk lokacin da kake masa nasiha shi a lokacin yake kara zafi,

   Aneesah tasaukar da murya tace " Bana son katafi, kazauna ni zanyi abba da momy magana, zan fahimtar dasu cewa bakason amal, kuma insha Allah zasu saurareni, kabani nan da kwana biyar"

  Afham yaja numfashi sannan ya ajiye akwatin akan gado yace "kwanar biyar kikace, nabaki, amma kisani cewa matukar ya wuce kwana biyar to tabbas zanbar gidan nan" yana karasa maganar yanufi hanyar bandaki,

   Aneesah tana murmushi, takarasa kusa ga akwatin, tadauketa takaita cikin drowar tasaka, koda tajuyo yashige bandaki,

   Kida kai tayi tana murmushi tabar dakin...
    *** ***
Bayan hilal yabar daki ameelah cike da zafin zuciya, airtel office yakoma, koda yaje sunkarasa komai, an rubuta duk wani detail akan number, yakarba yafara karantawa, mai number bama gari daya sukeba, nisa yake dasu sosai,

    Hilal yaja tsaki jiyakeyi kamar ya yaga pepar, miyakai ameelah waya da maza, meya rageta dashi meye baya mata, duk zuciyarsa yake yiwa wannan tambayoyin, saidai kuma ba amsa,

   Cen kuma wata zuciya tafara kawo masa wasu wasi,
  Ayya kuwa ameelah zata iya masa haka, tunawa yayi da irin soyayyar da sukayi abaya kafin aure,...

Na:- ❤Rabi'atu sk mash da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ
[1:17PM, 4/24/2016] ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
             ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ”…55and56๐Ÿ”…

Auren soyayya sukayi, baya tunanin ameelah zata iya cin amanarsa, (hmm baisan kuwa tagama ba )... cikin motarsa yakoma, yadafe kansa, yana tunin irin fadan da yayiwa ameelah, sai yaji duk tausayinta yakamashi,

    Yafi kusan minti goma cikin motar yana tunani duk jikinsa yayi sanyi,

  Sannan yakunna motar yadawo gida domin jiyakeyi kansa namasa ciwo, dakinsa ya wuce baiko gayawa ameelah yadawoba,

    Gado yasamu yayi kwanciyarsa,
     *** ***

Sai bayan la'asar lis ameelah tafarka, jikinta duk yayi tsami saboda dukan datasha,

  A kasale tatashi tanufi bandaki, tahada ruwan zafi tayi wanka,
  Jikinta yadan saki, tarage jin zafin bulalar, bata fito daga toilet dinba saida tayi alwala,

  Tana fitowa tayi sallah azahar da la'asar, domin bacci tayi bata samu damar yin sallar azahar ba,
   (Wa'iya zu billah, yan uwa mudaina wasa da sallah, sallah itace hisabinmu nafarko a ranar gobe kiyama, Dan Allah yan uwa mukiyaye)

Bayan ameelah tagama sallah, tatashi ta nade sallaya, ta ajiyeta saman gado sannan tanufi gurin mek up dinta,
  Motsi taji a falo, murmushi tayi domin tasan bakowa bane sai hilal, fushi yake da ita shine bai shigo dakintaba,

   Kwalliya ta chaba, wacca bata taba yiwa hilal irintaba,

   Bayan tagama ta kalli kanta ta mirror taga tayi kyau tai murmushi sannan tatashi, tanufi gurin shirinta,

  Wasu kananu kaya naga tadauko, tana kokarin sakawa, ( nan mukabar dakin muka fito waje, bayan minti biyar na leka dakin, ido na kafawa ameelah, wani irin kyau datayi)
 
  A hankali ameelah tafara zagaya dakin, kamar mai kowon tafiya,
   Tabbas tasan kwalliyar datayi danta janyo ra'ayin hilal ne zuwa gareta,

Cike da kinsa da karairaya tafito waje,

   A falo tasami hilal yana kallon wani indian fim, RAJKUMAR...

Tundaga nesa hilal yaji kamshin turarenta, ya juyo suka hada ido, yagagara dauke idonsa,

๐Ÿ”†NOTE๐Ÿ”†
Muna bawa Masoyan littafinnan namu AMANAR AURE, haquri zaku d'an jimu shru na kwana biyu! Da kuma masoyan HAFSATUL KIRAM, kuyimin uzuri insha Allah dana dawo zan qarasa muku! Muna godia da 'Kaunar littafanmu da kuke!๐Ÿ˜ƒ๐Ÿ‘๐Ÿป
   
Na:- ❤Rabi'atu sk mash da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ

Wednesday, 13 July 2016

AMANAR AURE

 ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ”…49 and 50๐Ÿ”…

Via OHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

A sandare hilal yakai xaune saman kujira, "innalillahi wa inna ilaihin raju un" itace kalmar dayaketa maimaitawa a bakinsa, Ya tafe qirjinshi da hannu

 yana mayar da nunfashi, gumi ya karwo masa, wani irin zafi yakeji a zuciyarsa, saboda tsananin kishi, idanuwansa sukayi jajir,
   A hankali ya dora kansa a jikin kujera, ya rufe edo, kalaman dayaji a wayar sukadai ke masa yawa a kwakwalwa,

  Cen bayan wasu yan mintuna ya bude idonsa, a lokacin hawaye suka sauka kan kumatunsa, yasa ya share,

  Wayar ya dauko yafara duba number, number airtel ce, ya fiddo da wayarsa yayi copy na number, sannan yasaka wayoyin duka biyu aljihunsa, yatashi yanufi dakin ameelah,

 wani dinkin atamfa yadauko mata tare da wani katon hijab, sannan yafito,
  Saidai ya tsaya ya rufe gidan kam sannan yashiga motarsa, airtel office ya wuce direct yabasu number suduba masa, suka ce masa saiya jira nadan wani lokaci, gudun karsu abba suga yajima baidawowa yasa yabar musu number tare da cemusu zai dawo anjima,

   Har a lokacin hilal yakasa dawowa hayyacinsa, jiyakeyi kamar zuciyarsa zasa fashe. Da zaiga wannan mutum da ya kira matarsa daya yayi mummunan saba masa,

  Hakadai yakarasa gidan malam mai ruqiyya a bakin kofar gidan kafin yashiga yatsaya ya daidaita kansa domin ba yason su abba sugane yana cikin damuwa, sannan yashiga cikin gidan, ya mikawa momy tunfafin,
       Abba da hilal suka fita momy ta chanzawa ameelah kaya, sannan suka dawo suna jiran farkawarta,
 
    Kusan rabin wuni sukayi a gidan, tun cikin dare har safiya ta waye, sai misalin 12:00pm na rana ameelah ta farka, a hankali ta bude ido tana kallon su momy da suke gefe da ita, bakinta na rawa tace "momy ina ne nan meya kawoni nan"

 murmushi momy tayi kafin takarsa gurinta tadafa kanta tace "ki kwantar da hankalinki, muna gurin nema miki lafiya ne "

Atsorace ameelah tace "lafiya kuma umma meya faru dani" momy tace " aike yakamata muyiwa wannan tambayar, meya faru dake a daren jiya ?"

Gaban ameelah yafadi domin ita harta mata da abinda yafaru da ita sai yanzu da momy tayi mata wannan maganar,
   Bakinta yadau bari, kamar zatayi magana sai kuma ta fasa, abba da hilal suna gefe suna kallonta, ameelah tace "nima bansaniba "

Na:-❤ Rabi'atu sk mash da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ
[9:49AM, 4/19/2016]
 ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ”…51 and 52๐Ÿ”…

ViOHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

Cike da mamaki momy tace "kamarya baki saniba?" Abba yayi gyaran murya momy tajuyo gurinsa, abba yace "kedaina tambayarta kijira ta samu natsuwa daga baya maji sauran zancen a gurin mijinta"

 momy taso tayi magana sai kuma tafara domin tasan tana musa masa zai hau masifa, saita kame bakinta,
   Suna zaune malam yashigo, yatarar da ameelah ta farka, godiya yayiwa Allah sannan yayiwa abba bayanin zasu iya tafiya da ita, taje cen gida takara samun natsuwa, abba yaciro bandur na kudi yabawa malam sannnan yayi godiya suka dauki ameelah,
   Gidan hilal suka wuce da ita, hilal yabude gidan suka shiga momy ta rikata suka karasa har cikin dakinta, saman gado ta ajiyeta sannan sukayi sallama dasu suka tafi,

   A mota momy tafara masifa anhata taji matsalar yarta wlh ba ai mata adalciba, abba shiru yayi ko kulata baiba yaci gaba da tukinsa, harsuka kasa gida masifa take, suna shiga harabar gidan abba yakashe motar ya rigata fitowa zuciyarsa cike da takaici ya nufi cikin gidan,
     *** **** ***
Hilal kuwa kamar jira yake su momy sufita, suna fita ya shigo dakin ameelah, tsaye yayi akanta yana kallonta, cike da bacin rai, fuskarsa a murtuke,

  Yana yinsa kadai ameelah ta kalla tagane cewa akwai matsala, taja jiki takarasa bakin gado, "mijina meya matsalar"
   Hilal ya tsuke fuska daman jiran yake tafar magana wayarta ya dauko yanuna mata, nan yafara fada cike da hargowa "daman abubuwan da kike aikatawa kenan a cikin wayarki, daman cin amanata kike.. Ehhh ameelah kifada mana?" yakarasa maganar cike da hargowa, da kuma zafin zuciya,

  Ameelah tayi rau rau da edo, tsoro yakamata matuka, kaku yasoma kubuce mata, muryarta na rawa tace "daman .... Ehmm..ehmm... "

" daman me Kifada mana, kifada.... Ya nuna kansa da dan yatsa "me kika rasa a gurina, kulawa, soyayyah, addini , ko kuma me, menai miki kike cin amanar aure na" yayi shiru yana jiran ameelah tayi magana amma takasa kuka kawai take,
  Hilal yadaga wayar cike da zafin rai "babu matakin dazan iya dauka akanki domin bazan iya sakin kiba amma nasan wannan ce koh, wannan ce matsalarmu koh, to daga yau babu ke babu kara rike waya"

Da karfi ya narka wayar a kasa, saida ta tarwatse gabaki daya,
  Ko uffan bai kara cewa ba ya juya yabar dakin yana huci,
 
Yana fita ameelah ta share hawayenta daman na munafincine, dukawa tayi tadauko fasanshiyar wayarta, taduba sim dinta taga yana nan, ajiyar zuciya tayi, tace "alhamdulillah, daman ni saki kawai nake tsoro, amma tunda baka sake niba, da sauki" tayi murmushi takara kallon wayar kafin tace " hilal kenan kaida kanka zaka kara siyomin wata nasan yadda zanyi dakai"

  Nan ta kwashe sauran fila2 wayarta ta ajiye gefe, sannan ta koma kan gado ta kwanta,
              *** ***
A gefen afham kuwa, tun lokacin dayayi yiwa amal wulakanci momy tai masa magana, tun daga ranar yake gaba da momy, ya daina mata magana, koya ganta saidai ya sunkuyar dakai ya wuce, duk abinda yakeso saidai yasa aneesah ta kawo masa, (hmm kunji yayan zamani masu gaba da iyayensu, yanzu hakan wasun suke, da zaran iyayen sun sun musu fada to shikenan gaba ta shiga tsakaninsu, su ala dole ba a musu fada, hmm Allah dai ya kyauta)

Momy ce zaune a bakin gadon dakin abba tana kallonsa yana shiri, hulla yake sakawa yana duban mirror,
  Damuwa ce tattare a fuskar momy tace "maganafa nake maka amma kayi banza dani, abubuwan yaron nanfa sunfara yimun yawa" tana karasa maganar tayi shiru,
  Saida abba ya kammala saka hularsa sannan yajuyo gurin momy fuskarsa a daure yace " afham yana ina" momy tace "yana dakinsa mana " abba yafara taku "zomuje " yanufi hanyar fita, momy uffan baka kara cewaba tabi bayan sa,
 
Direct dakin afham suka shiga, abba ya turo kofar da karfi yana kiran sunansa, yanajin shigowarsu ya mike tsaye, abba yatsaya yana kallonsa, afham ya sunkuyar da kai, abba yafara masifa "ka kyauta, kuma kayi daidai, wato kai dan zamani koh, kana gaba da mahaifiyarka saboda tayi maka magana akan Amal, to shikenan nima saika shirya yin gabar dani domin wlh bazan janye maganar aurenka da amal ba, idan zaka shirya kashirya domin munsaka ranar aurenku nan da sati daya, marar mutunci kawai " abba yakarasa maganar cike da bacin rai, yajuya yabar dakin,
  Kafin momy tafita saida ta dallawa afham harara, sannna tafita,

   Afham ya duke kai yana kuka, sai bayan sunfita sannnan yazauna yafara masifa "Allah dai yasani nidai banason amal, auren dole saikace wata macce, wlh bazai yuyuba saidai nabar musu gidan su zauna sukadai, kuma suje su samo wani dan su aura masa amal, wlh gidan zan bari...

Na:- ❤ Rabi'atu sk mash da Mr, Similes๐Ÿ˜ƒ

AMANAR AURE


 ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ”…45and46๐Ÿ”…

A hankali Ameelah ta fara bude idonta, momie na zaune gefenta tayi tagumi, ta miqe da sauri ta qarasa inda take!

Qarema dakin kallo Ameelah tayi kafin abinda ya faru da ita ya fara dawo mata a qwaqwalwa! A firgice ta miqe zaune, tasa hannu ta fizge qarin ruwan da akai matah sannan ta dora hannu akai ta fasa wata razananniyar qara, jikinta sai kyarma yake nan danan taa hada xufa tana wani irin kuka marar dadin saurare!

Su abba da hilal da suke zaune a waje sukaji karar ta da sauri suka nufo dakin..

Can muka hango momie maqale jikin bango ta dafe qirji cike da tsoro, daqyar ta iya bin bango har takai qofa nan suka hado da hilal da Abbah suna shrin shgowa tare da likita!

Momie kam bata bisu ba sai dai ta tsaya riqe da qofa, su Abbah suka qarasa inda take suna tambyarta meya faru? Sai mexai faru? Muryarta ko kadan bata fita! Sai wani zazzare edo take tana kallonsu, saikace bata sansuba, edonuwanta sunyi jajir, Har lokacin jikinta bai daina 6ari ba!

A tsorace likita ke mata gwaje2..
     Tashin hankali na hango muku sosae a fuskar hilal dasu Abbah, momie kam har ta fara kuka tana sambatu abinda ya qara qular da Abbah kenan!

Likita ya dade yana mata gwaje gwaje kafin ya fara musu bayani "gsky wannan aikin bana asibiti bne, rashin lafiyar Ameelah har yanzu mun kasa ganoshi, amma ina baku shawara kuje wuren malamai ku nema mata taimaka!

Momie ta dafe kirji tace "na shiga uku! Wannan wane irin ciwo ne, Allah wannan sammu ne aka mata, ture ne za'a mata, domin mu duk danginmu babu mai jinnu! Koma waye sai Allah ya saka miki!

Abbah ya watsa mata harara yace "don Allah ki shga goma ba uku ba, lafiyar 'yerki zaki nema ko kwasar ma kanki zunubi xaki tsayayi wurin zato?

Daukar Ameelah zamuyi mu koma da ita can gidanmu mu nema mata magani? Ta daga kai tana gurnanin kuka cike da tausayin 'yer tatah!

Na:- ♥Rabiatu sk msh da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ
[4/17, 12:55 AM]
๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ”…47and48๐Ÿ”…

Daga asibitin wurin wani babban malami mai bada taimako suka wuce, sun mishi bayanin abnda ke damunta malam yasa almajirinshi ya kawo mishi ruwa a kofi ya tofa mata addu'o'i a ciki sannan ya watsa mata a fuska, tai wani irin zabura ta fara ihu da kyarmar jikin, nan malam yaci gaba da mata ruqiyya!

Duk yanda yaso Ameela tayi magana ko kadan bata fita, bugu (duka) kam ameelah ta shashi duk ta qara fita hayyacinta! Gata fara fatar jikinta tayi jaa sosai da manyan borarai,
     Daqyar aka samu kafaffen Aljanin ya fita, nan ta kwanta ta fara nannauyan barci!

Hilal duk da yana namiji sai da ya zubda mata hawaye, ji yake kamar ya maida ciwon jikinshi saboda tsananin tausayin matarshi, momy ma kuka take cike da tausayi, wani duka akayiwa ameelah shi saita rufe ido, saboda ihun da ameelah keyi,
    Abbah ne ke qarfafa musu gwiwan basu haquri yana kwantar musu da hnkali! (Su Ameela kam anji jiki, ko wannan ya isheta darasin cin Amanar Aure??)

Tufafin dake jikin ameelah duk sun lalace,

Abbah ne yace ma hilal yaje ya dauko mata kayanta saboda daga nan idan tafarka gida zasu wuce da ita saita qara samun sauqi! Jikinshi a sanyaye ya tafi cikin tunanin halin daya bar Ameelah!

Sai da yaje gidanne ya iske a bude kamar yadda ya barshi, yananan ynda suka barshi, qafarshi yaji ya daki wani abu akasa, ya duqa wayar Ameelah ne ya dago yana dubawa kusan 9 miss calls.

Bai duba ko na waye ba yana shirin ajewa wani kiran ya qara shgowa! "HMM" yaga an rubuta, ya dauka ya kara a kunnenshi yana shirin magana.. Hmm ya rugashi!

Cikin tattausan murya yake magana "haba! Haba!! Haba!!! My Ameelah ni babu abnda zaki cemun, kinsan yanda na shaqu dake bzanso kimin nisa ba koda na qaramin lokaci ne, ya za'ay ki brni tun jiya ba chat ba waya? Yayi shru yana jiran abnda zatace.

Shikau hilal mutuwar tsaye yayi da waya a hannunshi, ko motsi yaa kasayi! HMM yaci gaba "ya zaki shru ki qyaleni masoyiyah? Kinsan irin son da nake miki ko kin daina sonah ne? Nasan hkanma bzai yiwu ba amma kimin magana ko zanji dadi a raina!

Shi kadai yake magana yana qara ma hilal quncin zuciyah! Shi da kanshi ya gaji ya kashe har lokacin hilal yaa kasa cire wayar a kunnenshi yayi tsaye kamar wanda aka dasa!

๐Ÿ”†kuyi haquri plz da rashin jinmu kwana biyu dabaku yiba, duk muna exam ne๐Ÿ‘๐Ÿป Masu neman na bayanma su mana uzuri plz๐Ÿ”†

Na:-♥Rabiatu sk mashi, da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ

AMANAR AURE

๐Ÿ˜ƒ: ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
             ๐Ÿ”…41 and 42๐Ÿ”…

Via OHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

Ameelah tayi rau rau da ido kamar mai shirin yin kuka, ta daura hannunta akan kypat tafara typing

Ameelah "waye dan Allah, menai maka na zagi"

New no " ni bawan Allah ne kamarki amma ba irin jinsin kiba, ni aljanine, yanzu haka duk abinda kike yi ina kallonki, watar Allah ukubar Allah tana tattare da macce mai hali irin naki, yanzu haka ina kusa dake, la'ananna wacce bata san darajar Amanar aure ba"

     Bashiri ameelah ta fara duba gefe gefen ta cike da tsoro tatashi tsaye, tana kallon falon,

  Saida Ta tabbatar da komai aciki sannan tamayar da edonta ga wayar tana duba sakon daya turo, tsaki taja a zuci take fadan "wannan yama rainamin hankali, ni zaicewa ba mutum bane,  
   Cike da bacin rai da kuma raini tafara masa reapply

Ameelah "to idan kai ba mutum bane kafito naganka, ko angaya maka ni matsoraciyace "

New no " hahaha ai bazan fito kigan niba domin ku bil adam bakuda karfin halin ganin tsarin halintarmu amma zan taba kyankyawan gashin nan naki ki tabbatar da cewa ina kusa dake "

Ameelah "๐Ÿ˜ก eh nayarda kataba din...mtsw"

   Taja tsaki tana kokarin rufe data taje ta kwanta domin taga karfe 3:10,
  Ta rufe Datar tayi tsaye tana tunanin mutumen,
 
   Jitayi an fizge gashinta da karfin tsiya, wata irin mahaukaciyar ihu tasaka, ko juyowoba bata yiba tafadi kasa somammiya,
( nida nake gefe saida birona yafadi, saboda tsoro, koda naduba gefen abdul shiharyakai bakin kofar fita daga falon, lolllx ...nayi kamar nabisa amma sainace to idan nabisa yazaayi nasan halin da ameelah zata shiga saina tsaya)

Kamar daga sama hilal yajiyo ihunta a cikin baccinsa, a gigice ya farka da sunan ameelah a bakinsa, yaduba bata kusa dashi, a gigice yatashi ya nufi bandaki, yaga bata ciki da gudu yafito yanufi falo,
   A kwance yasame kasan cafet, da gudu yakarasa gurinta ya daga kanta yana girgizata yana kiran sunanta amma shiru, ya daura hannunsa a akan hancinta yaji bata numashi, a gigice yatashi yakoma daki yadauko makullan mota, yafito ya tallabota, ko takalmi babu a kafarsa, yafita waje a mota yasakata gidan baya, sannan yayi sauri yaje ya bude gete yadawo yashiga motar ya tada motar yafita, bai tsaya kulle gidan ba adu ar fita daga gida yayi yabarwa Allah sarkin iko... Domin yayi ikonsa akan gidan nasa,

Na:- ❤Rabi'atu sk mash da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ

๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
             ๐Ÿ”…43 and 44๐Ÿ”…

Via OHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

  Wata karamar asibiti ta tabayan layinsu nan ya dosa, a manne yakarasa asibitin, ya kashe motar ko cire keys bai tsayaba yazagaya ya dauko ameelah ya tafito da ita daga cikin motar yamayar da kofar motar ya rufe, yanufi cikin asibin a gigice yake tafiya yana kiran sunanta, amma bata motsaba yana isa cikin asibin likitoci suka karbeta, suka nufi emergency room da ita, hilal yayi kokarin shiga dakin amma suka hanashi, wuri yasamu agefe yazauna ydafe kai yana hawaye tambayar kansa yake "meya faru da ameelah Allah katada kafadunta"
  Zufa ya karyo masa yasa hannu ya shafe,...
 (Bawan Allah hilal, abin tausayi, matarsa sai ci masa Amana take, da sannu Allah zai saka masa)...

Lalluben aljihunsa yafarayi, yafito da wayarsa ya kira iyayen ameelah,

3:40am
Suka karaso asibitin, yana ganinsu yatashi tsaye suka karaso gurinsa, a gigice momy tace "meya faru da ameelanah.. Hilal meya faru da ita"

 hilal ya girgiza kai "momy wlh nima bansanibah kawai nazo naganta akwance ne a falo"

Cike da mamaki momy tace "falo kuma, tokai kana ina" hilal ya bude baki zaiyi magana abba yace "yanzu balokacin wannan tambaye2 ne ba, kuzo muje muji me likitoci zasu fada akan" abba yafice momy ta kalli hilal kallon rashin fahimta sannan tabi bayan abba, hilal ma yabi baynsu...

Sunfi minti 29 a bakin dakin da Ameelah take ciki sannan likita fito, da sauri suka taresa,

abba yace " likita meke damunta "

likita ya dube abba, momy and hilal yace " babu abinda ke damunta sock ne kawai akwai abinda ya firgitata, tasana diyarsa tasamu sock, amma batada wani matsala kowanne lokacin zata iya farkawa, idan ta farka kuma tana bukatar hutu kafin kuwuce da ita gida"

abba yace "alhamdulillah, Allah mungodema, ya juya gurin likitin "yanzu likita zamu iya shiga muganta "

 likita yace " a a ba yanzuba kujira harta farka, ko kuma dayanku yashiga domin idan tafarka taga wadda tasani kusa da ita, kota samu natsuwa "

   Momy tayi saurin cewa "nizan shiga likita" abba ya juyo ya kalleta, zumudin nan nata bata masa rai yake, ya harareta amma ko a jikinta, bata jira likita yayi maganaba ta tsunduma cikin dakin,
  Likita yace " ita kadai ta isa ku sai kuzauna acen kafin tafarka" ya nunawa abba wuri da hannunsa sannan yafice yabar wurin,
  Abba da hilal suka samu guri suka zauna suna jirar farkawar ameelah...

Na:- ❤Rabi'atu sk msh da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ

AMANAR AURE

๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
             ๐Ÿ”…37 and 38๐Ÿ”…

Via OHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

Hilal yashigo dakin yayi tsaye yana kallonta, yanayin yadda tayi kwanciya yasa yaji aransa kamar tanada gajiya a tattare da ita hakan yasa bai tada taba,
   Wurin cire kayansa yanufa ya cire tufafinsa, jallabiya ya janyo yasaka, sannan yanufi gado, har alokcin saida yayita kallon ameelah, yau cike yake da sha'awarta amma bazai takura mata ba, murmushi kawai yayi, ya kwanta ya janyo bargo, a hankali ya karanta addu oinsa na bacci sannan ya rufe idonsa,
    Duk abinda ykeyi ameelah najinsa amma saita basar, kamar bacci take
  Kusan awa daya tana kwance amma bacci take ba,
   Sannan tatashi tayi mika tana kallon hilal, amma duk da hakn bata tashiba, sunansa tarika kira a hankali, taga ko motsawa baiba hakan ya tabbatar mata da cewa yayi bacci, sannan tatashi a hankali, tana tafiya cikin sanda harta fita daga cikin dakin,
  Daman wayarta na falo tana chaji, wurin wayar tanufa ta dauko wayar tadawo saman kujera tazauna, agogon wayar ta duba 11:30, wani irin dadi taji domin bata saba alkawarin datayiwa Hmm ba,
   Data ta bude cike dajindadi, massages suka fara shigowa, saida tajira suka gama shigowa kaf sannan tafara shiga whtsapp, bunbude sakonan takeyi ahankali tana yin reapply, hartakai ga number hajna beauty,
  Dubawa tayi taganta tana online, ai kuwa nan suka fara chart hajna tayi mamaki sosai ta yadda taga ameelah tana matsayin matar aure amma tana chart din dare, har kusan 12..


   11:56 Hmm ya shigo online, tana cikin charting da hajna taga text dinshi yashigo, da sauri tafito daga cikin hajna tadawo cikin hmm sakone yaturo

Hmm "Gaskiya beauty ina matukar jinki a raina, ta yadda kike cika mini alkawari"

Ameelah "hmm bakomai ai danna faran ta maka nake",

Hmm "๐Ÿ˜˜ thnx i love yhu, ina jinsonki harcikin zuciyata, gaskiya bazan iya hakura dake ba, sonake kizamo mallakina"

Murmushi ameelah tayi kafin tafara typing

Ameelah "๐Ÿ˜€toh meyasa kakeson nazamo taka"

Hmm "hmm beauty kenan saboda ina sonki mana, wai kinkosan yadda nakesonki, bana iya minti talatin batare da ka kalli pic dinki ba"

Ameelah "๐Ÿ™ˆ toh lallai kana sona sosai to idan nazamo mallakin wani fa"

Hmm " ๐Ÿ˜ก aikuwa wlh dasai nakashesa, kuma kisa hallahira"

Ameelah "๐Ÿ˜ณ kisa kuma, kana nufin zaka iya kisa akaina kenan"

Hmm "sosai ma kuwa wlh idn har akace za a rabani dake to baa nemi zaman lafiyaba"

Ameelah tayi dariya a zuce take fadan wannan baida hankali, inajin ya zauce, nadi nake matar aure taya zaiyi wannan ikirarin akaina, ni wannan soyayyar tamu a whtsapp kadai nadauketa amma banda zahiri,
  Murmushi tayi sannan tafara reapply

Ameelah "๐Ÿ˜ƒ๐Ÿ˜€ toh idan nice nace bana sonka fah, yaza kayi "

Hmm "๐Ÿ˜ก๐Ÿ˜ก๐Ÿ˜ก kidainamin irin wannan wasar, babu abinda natsana a duniya irin yaudara, budurwa ukku nayi kuma kowacce nina kasheta da hannuna saboda ta yaudareni, beauty idan kema kika yaudareni, kasheki zanyi sannan kuma nakashe kaina, domin nasan dacewa nazo duniya da rashin saa, bantaba jin nakamu dason macce kamar ydda nakamu dasonki ba, Dan Allah beauty karki yaudareni,.domin bana bashin yaudarah"

Tun bata gama karanta text dinba tasoma jin jiri, wani zafi taji yafara fita daga jikinta, dukda fankar datake cikin falon, amma bata hana zufa yakaryi ta jikin ameelah bah,

  Wani iri tsoro taji yakamata, ayya kuwa wannan mutum ne, hannunta tadaga tana dan fifitawa jikinta,...
    (A zuci nace su ameelah angamu da ...๐Ÿ˜ก๐Ÿ˜ก)

N:- ❤ Rabi'atu sk msh da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ
[4/10, 12:03 PM]
๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
             ๐Ÿ”…39 and 40๐Ÿ”…

Via OHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

Cike dajin tsoro tafara typing

Ameelah " Dan Allah da gaske kake kataba kisa akan yaudara, kodai wasa kakemun"

Hmm "๐Ÿ˜Š beauty kenan ai babu wasa a cikin maganata, ni makashi matane masu yaudara, amma idan kina tattama jirani kigani"
 
 Gaban ameelah yafadi sosai tace nashiga ukku, motsi tajiyo a bakin kofar dakin da hilal yke kwnce,  
        Cike da jin tsoro ta juya gurin, bakomai bane kofar dakin ne tayi kuka, domin ta manta dazata fito bata rufe kofarba, a hankali tayi ajiyar zuciya sannan tatashi taje ta rufe kofar tadawo tazauna, tadauki wayarta..
      Images tagani guda ukku sunshigo, a hankali tasaka download dinsu, nafarko wata kyankyawar maccece, a kasan pic din an rubuta "wannan itace SAJIDA itace budurwata ta farko, ta yaudareni kuma na kasheta" kuma babu abinda kayi..

  Ameelah ta zare ido a zuci take fadan innalillahi wa inna ilaihi raju un",

  Pic nabiyu yabude a hankali tasa hannu ta dannan cikin pic din yabude, shima photon maccece amma bata kai kyau ta farin ba, a kasan photon an rubuta "wannan sunanta FARIDA, munhadu da ita ne ta Facebook, munkusan share wata biyu muna soyayya hartakaimu gamun hadu a fili, data ganni shine tace bata sona, a take gurin zuciyata tahau na kasheta halla hira"

  Cab jekaga zufa a jikin ameelah, idanuwanta sunfito bulla2, jikin ta har wani rawa yake,
  ( nace " ameelah tahadu da jafa i, hmm farawace idan har bata daina cin AMANAR AURE ba, )

   Hannunta narawa ta danna cikin photon na ukku, tashin hankali ๐Ÿ˜ณ Gawar maccece anyanka mata wuya gata akwace cikin jini, ameelah jitayi kamar ta burma ihu, (koni da nake gefe saida nakasa tsayuwa, saida bro Abdul yacemun "be a man plx" sannan na tsada hankalina naci gaba da rubutu)

  Ameelah takasa tsayawa ta duba abin aka rubuta a kasan photon, domin tataba ganin photon a wani grp nata na whtsapp akace wani yakashe budurwarsa saboda ta yaudareshi,

   Zuciyarta duka takeyi sama sama, a akan photo nan text ne kusan guda shida, a tsorace tafara karantasu,

1, wadan nan sune matan da suka yaudareni,

2, a yanzu haka babu ko daya a duniya

3, beauty karki yaudareni domin bazan iya hakurin rashin kiba

4, koda yake ai nasan kina sona bazaki yaudareniba

5, ina fatar kinfahimci maganata ko beauty, karfa kiji tsoron halina niba mugu bane, kuma bana cutawa kowa sai wadda ya cuceni,..

Kafin tagama karanta text 5 taji karar shigowar wani sakon a waje, bakuwar number data gani dazuce akayi mata text da ita,

  A hankali ta duba agogon dayake saman screen na wayarta karfe 2:31 tagani, duk tsoro yakamata
 Sannan takaranta text nashida

6, nasan yanzu kin tsorata dani. Dan haka zanbarki kije kiyi bacci kisamu natsuwa, Saida safe. Nyt swt drm my beauty๐Ÿ˜๐Ÿ˜˜ "

   Saman sunansa taduba taga last seen dinsa kusan minti biyu da saukarsa, bata masa reapply ba tafito, bakuwar number data gani wadda akayi mata text kuma number bata nageriya bace sakon takai hannu ta danna sakon ya bude, sakone kamar haka " ke dan kutumar banki ya inai miki magana kin wani shareni, bana son iskanci fa" .....
  (To wata sabuwa inji yan chacha)

Na:- ❤Rabi'atu sk msh da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ

AMANAR AURE

 ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
              ๐Ÿ”…33 and 34๐Ÿ”…

Via OHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

kai tsaye garden ya wuce cike dajin haushin Amal, wayarshi ya fiddo yana addu'ar Allah yasa Ameelah na online ko fira suyi ya samu natsuwar zuciyarshi,

Cikin rashin sa'a kuwah bata online tsaji yaja, ya tura wayar cikin aljihu sannan ya lumshe ido, kamannun ameelah yafara bayyanowa a cikin zuciyar yana murmushi, tunanin ameelah kadai ya isa yasaka shi farin ciki,
        *** ***
Sai bayan la'asar lis sannan hilal yafita, bayan duk mai wakana ta auko tsakaninsa da matarsa ameelah, sabon wanka yasake tare sukayi wanka shida ameelah, yaudaikam yasamu farin ciki sosai a gurin ameelah, basu fito daga bandakinba saida sukayi alwala, suna fitowa hilal yajasu sallah, bayan sungama yafita...

Ameelah tafita tarakashi har waje, sannan tadawo cikin Falo yanayin Falon ta kalla yadda yayi kaca kaca, tayi ajiyar zuciyah, sannan tashiga gyara, komai batayi acikin gyaranba taji wayarta tayi karar shigowar text, da sauri ta ajiye aiki tanufi wuri wayar,

Sakon afham tagani, magiya yake mata akan dan Allah ta hau online, yayi miss dinta,

Murmushi kawai ameelah tayi, ta janyo data ta bude tana jiran shigowar massages,
          *** ***

 Afham yana zaune yaganta online wani dadi ya kama zuciyarshi don yanason chart da Ameelah, nan take ya manta da bacin ranshi cikin nishadi yake mata typng..

Afham "Ina fatan kyakkyawar mace ma mallakiyar zuciyatah tana cikin qoshin lpy.

Murmushi Ameelah tayi cike dajindadi

Ameelah "lpylau kaipa?

Afham " ina cikin Annashuwa dajin dadi, Ameelanah yau babu wanda ya kaini farin ciki, gsky nazo duniya cikin sa'a dana hadu dake๐Ÿ˜˜

Ameelah " 'nima nayi sa'a kuma ina cikin farin ciki"

 Afham "kinsan me? Inanan zaune nake a garden ganyayyakin itatuwa sai kadawa suke ga daddadan iska mai dadin shaka, ji nake dama muna tare! Don Allah Ameelah yaushe zamuyi aure??

Ameelah tazare ido, kafin tayi ajiyar zuciya

Ameelah "da wuri haka? Duka yaushe na sanka? ko soyayya bmu fara bapa"

Afham yayi murmushi, yana kallon text din ameelah azuci yake fadan, da ameelah tasan yadda yadamu dasuyi aure da wuri dabata fadi hakanba, kodan yabakan tawa amal zai nemi auren ameelah da wuri, bayan yadawo duniyar tunanin daya shiga yafara typng...

Afham "miye a cikin soyayyah Ameelah? Zamu dinga chart ne ko waya, kullum tambyr bazata wuce ya kke? Kinyi mafarkina? Gsky hotannan kinyi kyau sosae! Hmm wannan bashine soyayyaba, ni Kullum burina in kasance tare dake, amma sai dai ayita musayar kalamai ana bayyana shauqi, mezai hana muyi aurenmu kawai?

Gaban Ameelah ya fadi, lallai Akwai rigima, tana cikin tunanin text dn Afham ya kara shigowa
    Yace "son gaskiya nake miki Ameelah sona aure, idan kina ganin biki sanni ba ko banyi miki ba zan miki bayanin komi a kaina ga hotunanah nan, don Allah Ameelah ki zamo tawah karki gujemin!

Ajiyar zuciah tayi bayan ta gama karantawa duk ta hada zufa, hotunanshi ne take kallo ta jinjina kai a fili tace gaskia Afham kyakkyawan gaskene!

Yayi matuqar burgeta, nan tafara saqe saqe a zuci, ji take daman Afham ta fara haduwa dashi kafin ta auri hilal,

Na:- ♥Rabiatu sk mashi da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ
[4/7, 1:18 AM]
 ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ Amanar Aure๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
             ๐Ÿ”…35 and 36๐Ÿ”…

Via OHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

Ranar sunyi chatn sosae da Afham ana shirin yin sallar magrib yasauka yace itama taje tayi sallah, amma taji har akayi sallar magrib tana zaune, sai bayan angama sannan tatashi tayi sallar, bayan tagama tana tatashi tadauki wayarta tasaka chaji amma ta gagara ajiye wayar sai duban DP din frds dinta take har lokacin da hilal ya dawo babu Abnda Ameelah tayi, sai da taji tsayuwan motarshi ta ajiye wayan da sauri ta fara gyaran dakin...

Da leda ya shigo a hannushi ta amsa ta mishi sannu da zuwa ya qarema dakin kallo yanda ya barshi haka ya iskeshi, tana shafar kai tace "tunda ka tafi nake bacci ban samu nayi komai ba gidan!

Hilal yiyi murmushi
    Yace "ay kara ki dinga hutawa, bari in fito in tayaki shara! Tayi murmushinta ya shge bedroom dinshi shima babu abnda ta gyara, haka ya shga toilet watsa ruwah shima ko wanki babu (sis rabi'at itama datake macce saida tace wannan wane irin jarabar chatn ne? Wasu matan zasuyi chatn bzasu gyara gdansu ba, babu ruwansu da tsaftar yaransu ko girkin mai gida! Sun gwammace su hau chatn suna cin Amanar aure, ko kuma chatn da qawayensu yaafi musu, nace "gsky ne ba duka matan ke da wannan tunanin ba)

Cikin sauri tashiga gyara gidan kafin ya fito, bayan yafito yazo yatayata suna aikin suna fira babu jimawa suka gama, ana kiran salar isha, hilal yafita yaje masallaci,

Yana fita, kamar tana jira, dasauri takoma gurin wayarta, daman datarta abude take, sakon ni taga sunshigo da yawa, harda wata bakuwar number, ta tsaya tana kallon number, number kamar bata Nigeria ba, saidai kuma hello kawai akace acikin number, saida ameelah takarewa number kallo sannan tafito, lambar hmm tagani ya auko mata sako, tayi sauri tashiga taduba, yace "beauty nayi miss din kalamanki dan Allah muhadu shabiyun dare akwai wani kyankyawan albishir dazan miki, plx kihau karki cemun kin manta saimun hadu" tayi ajiyar zuciya, kafin tafara zancen zuci "yanzu yazaayi muhadu, inason naji albishirin nan nasa" saikuma ta kada kai tace yes natuna,(na kalli rabi at nace "sis mekuma ameelah ta tuna ", tace "oho.. Musa ido mugani" nace "tomh)

Tana zaune tatuna da sallah dasauri tatashi tanufi bandaki bayan tafito tafara sallah, kamar wadda aka saka yin dole shaf shaf takarasa, tatashi ta nade sallayar sannan tafara shirin bacci kafin hilal yadawo,

Bayan ta kammala shirinta tafesa turare, sannan takoma kan gado ta kwanta, tanajiran dawowar hilal,

  Kusan mintinta ashirin a kwance tana jiran dawowarsa, jitayi anturo kofar dakin, tunkafin yakarsa shigowa tayi saurin gyara kwancinta, sannan tarufe ido, tafara jan minshari.....

Na:- ❤ Rabi'atu sk msh da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ

AMANAR AURE

, ๐Ÿ’ ๐Ÿ’  Amanar Aure ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
           ๐Ÿ”…29 and 30๐Ÿ”…

Via OHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

Favorite food dinta yasaya mata tuwon amala da miyar yakuwa,
   Zauna tayi ta gyara cikinta, taci saida ta koshi sannan tatashi, taje kichin ta wanke hannayenta tayi drooping din ledojin a dustbin,
   Ta wuce dakinshi kai tsaye,

   tatura kofar dakin tashiga sannan tayi sallama, a kwance tasamesa saman gado, dagashi sai singlet sai gajeren wando yayi shirin bacci,

   Batare daya ko motsa daga kwanciyar dayakeba ya amsa mata sallamar.

   Sum2 ameelah takarasa bakin gadon ta zauna tana facing dinshi,
   Tayi gyaran murya tace " fushi kake dani mijina"

    Baikulata ba hasalima juya mata baya yayi,

  Sai abin yasoma bawa ameelah dariya domin tasan hilal bazai taba fushi da ita,.ba. ( a zuci nace "oooh shiyasa takecin Amanarsa. Dan taga yana sonta, da karfi naji an firgi biro daga hannuna, "idan kingaji da rubutun kibani naci gaba" Bro abdul yafada ransa a bace, na shagwabe masa fuska kamar zanyi kuka nace " haba dan Allah nina cemaka nagajine. Tunanin wani abu kawai nake" sai yace "to naji karbi amma karki sake" nayi murmushj na karbi biron naci gaba da rubutu" ...
        *** ***
Ameelah takara matsawa kusa dashi, ta dora hannunta a bayansa, tasaukar da murya "Dan Allah my heart beat kayi hkr, nayi maka alkawarin baxan karaba insha Allah"

   Hilal ya juyo yana murmushi suka hada ido, ameelah tamayar masa da amsar murmushinsa, sannan ta lumshe, a lokacin daya kama hannunta yana shafar tsakiyar, hilal yace "kinyimun Alkawarin baxaki karaba, to idan kika sake fah"

 A hankali ameelah ta bude ido tace "kayimun duk hukunci daya dace dani"

  Hilal yayi murmushi yace "to shikenan uwar yayana, Allah yakara bamu ikon hakuri dajuna"

 ameelah ta amsa da murmushi "Ameen mijina"

  Cikin wasa Hilal ya matse mata hannu, Ameelah ta saka ihu kadan,

dariya yayi sosai, yace "matsoraciya, sai raki"

Ameelah ta shagwabe fuska tana yarfa hannun "Allah ni saina rama, haka kawai zaka jimun ciwo dan kaga baikai karfin kaba"

  Hilal yatashi zauna, ya kura mata ido yana murmushi " tohm kirama mana idan kinada karfi" ya daga mata edo,

ameelah tace " to mikon hannunka"

hilal ya mika mata hannu, ameelah ta rike hannun taje ta matse hannun yayi mata dabara yakara matse mata hannu ta kara saka ihu, dasauri ya sauko daga kan gadon yana dariya sosai, ameelah tatashi tsaye tayo kansa tana gunguni. "Allah ni bazanyi hakuriba saina rama duka biyun" tana kokarin karasawa gurinsa yana janyewa, hardai abin yazamo musu wasa...
  (Toh nidai naja birona, da littafi nafita, nacewa mr smiles shima yafito mubar musu dakin domin wasar tafara karfin da dazan iya rubuta waba, wasan maaurata, dole muka fito mukabar musu daki, muka dawo falo muka zauna muna jiran sugama wasar mucigaba da rubutu, wasa2 abin har muka kusan awa daya ba labarin fitowarsu, abdul yace "ke tashi muje nina gaji da jiran wadan nan muje gidan su afham muje muga wace wainar ake toyawa, ban musa masa ba domun nima nagaji da jiran, fita mukayi muka lula garin gombe...)
    *** ***
Katon hijab tasaka sannan takawo safa ta rufe kafafunta da hannayenta, kyankyawace duk da babu kwalliya a fuskarta, fuskarta mai cike da kamala, annuri, da kuma haske, ....

Wacece wannan.... (Na tambayi bro Abdul)...

Na:- ❤ Rabi'atu sk msh da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ
[11:17AM, 4/3/2016]
 ๐Ÿ’ ๐Ÿ’  Amanar Aure ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
            ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’ 
           ๐Ÿ”…31 and 32๐Ÿ”…

Via OHW๐Ÿ“ฑ๐Ÿ“š

AMAL kenan, yarinya mai hankali da natsuwa ga son addini, ta turo kofar falon tashigo, aneesah da Ammi suna zaune a falon amal tashigo, aneesah ta tashi tana murna ta rungume amal, Ammi datake gefe tana murmushi tana kallonsu, bayan aneesah tasaki amal,
  Amal ta sukuyar tagaida Ammi,
   Ammi ta amsa cike da jindadi, sannan tatashi tabar musu falon, bayan sun zauna,

  Aneesah tace " ya ustaxiya, ke kullum kinrufe jiki da katon hijab saikicevwata matar aure dubi dan Allah duk zafin nan kinsaka safa"

  Amal tayi murmushi wadda yakara bayya dimples dinta "eh naji, komai zaki fada kifada, addinin mu yasanar damu cewa duk ilahirin jikin 'ya macce al'aurace bayan fuskarta da kuma tafin hannunta, kingakoh yazama dole narika rufe duk wata al'aura datake jikina"

 Aneesah ta tabe baki "aikuwa daman nasani ana fara miki magana zaki fara yiwa mutane wa'azi "

murmushi amal tayi ta girgiza kai tace "hmm ai yanzu duk duniya tazama daya gaskiya wuyar fadane da ita, ida kuwa ka kuskura kafada to yanzu za'a rika kiranka mai waazi, karfa kimanta a cikin suratul AHZAB aya ta hamshin da tara 59 Allah subhanahu wata ala yana cewa, " ูŠَุง ุฃَูŠُّู‡َุง ุงู„ู†َّุจِูŠُّ ู‚ُู„ ู„ِّุฃَุฒْูˆَุงุฌِูƒَ ูˆَุจَู†َุงุชِูƒَ ูˆَู†ِุณَุงุกِ ุงู„ْู…ُุคْู…ِู†ِูŠู†َ ูŠُุฏْู†ِูŠู†َ ุนَู„َูŠْู‡ِู†َّ ู…ِู† ุฌَู„َุงุจِูŠุจِู‡ِู†َّ ุฐَٰู„ِูƒَ ุฃَุฏْู†َู‰ٰ ุฃَู† ูŠُุนْุฑَูْู†َ ูَู„َุง ูŠُุคْุฐَูŠْู†َ ูˆَูƒَุงู†َ ุงู„ู„َّู‡ُ ุบَูُูˆุฑًุง ุฑَّุญِูŠู…ًุง " O Prophet! say to your wives and your daughters and the women of the believers that they let down upon them their over-garments; this will be more proper, that they may be known, and thus they will not be given trouble; and Allah is Forgiving, Merciful" " Yaa kai Annabi! Ka cewa matan aurenka da 'ya'yanka da matan muminai su kusantar da qasa daga manyan tufafin dake a kansu. Wancan yafi sauqi ga a ganesu domin kada a cucesu. Kuma Allah ya kasance mai garafa ne mai jin qai"

  Aneesah taja nunfashi tace "Allahu akbar, nidai yanzu kiyi hkr zanma zo kikoyamun irin wannan shigar taki, nima naxamo ustaxiya" takarasa maganar tare da makkale murya, aneesah taci gaba da cewa " yanzu dai kitashi muje nakaiki ki gaida yaya afham yana cikin dakinsa, domin nasan wurinsa kikazo"

   Amal ta sunkuyar da kanta cike da kunya, aneesah tazo ta kama hannunta suka nufi dakin Afham"

Zaune yake a kan wata kujera datake cikin dakinsa sanye yake da yadi fari, wadda yayi shara2 sosai, daga nesa zaka iya hango singlet dinda kejikinsa, yayi matukar kyau, photon ameelah yake kallon yana murmushi..

Amal ce tafara shigowa cikin dakin tare dayin sallama "Assalamu alaikum warahamatullahi ta'ala wabara katuh" complete ta cika sallamar, hakan yasa Afham ya chanza yanayin fuskarsa, domin yagane ko wace, tun a gurin sallamar,

   Kamar bazai amsaba saikuma ya amsa ciki2,

Aneesah tace "to tunda munzo ni bari nakoma nashirya miki abinci kafin kifito"

Cike da kunya Amal tace toh shikenan"
  Nan aneesah tafita tabar musu dakin,
  Shiru amal tayi tana tunanin mezata cemasa..

Maganar sace ta katse mata tunani, cike da bacin rai yace "lafiya meya kawoki dakina"

 Amal tace "gaisawa kawai naxo muyi"

Afham yace " to shikenan mungaisa, saiki tafi koh"

Amal tayi gyaran murya tadaga edo ta kallesa, a ko wane bugun zuciyarta kara son afham take, amma tarasa dalilin dazaisa ya tsaneta,

 Amal tace " ya Afham meyasa kake wulakantani, nifa mutumce kamarka, kuma yar adam kamarka amma narasa dalilin dazaisa karika wulakantani, dan Adam fa abin karramawane koda kuwa baka sansaba, balleni danake yar uwar, Allah subhanahu wata'ala yana cewa nakarrama dan adam fiye da kowace halinta datake doron duniya, yaya Afham kasani cewa..."

Afham yadaga mata hannu ransa abace, "ya isa haka, naji kuma nayarda, matsalar ki kenan daga anfara magana sai kifara wa'azi, ni ko wannan wa'azin naki yana daya daga cikin abubuwan da banaso, saikace wacca aka haifa agaban littantanfan islamiya, Afham yakara kallon irin yanayin shigar Amal, yaja tsaki yace "lok amal nifa tsarinki kwata kwata baimunba, ke gabaki daya local ce baki wayeba" yatashi tsaye yana nuna mata dan yatsa kamar zaikai mata duka "dubi yadda kike shigarki saikace yar gafaka, dan Allah Amal ki hakura dani, kinji ance kwarya tabi kwarya kibarni nasamu daidaini kema kije kisamu daidai ke"

  Amal hawaye take sosai, tana danasanin zuwa dakinsa datayi, daman tasan wulakancine tukwauicin dazata samu, dolece tasa tazo saboda son datake masa,

   Yaja tsaki yanufi hanyar fita, a bakin kofar yaci karo ammi dasauri yaja da baya, ammi takarasa shigowa dakin ta kalli amal sannan tajuya ta kalli afham ta bata rai sosai tace "daman nasan za'a rina, hakan yasa nabiyo bayanta domin nasan halin wannan bakar zuciyar taka, inajin duk irin abubuwan dakake fada mata, ka kyauta mutumen bazan, wadda bayajin maganar iyayensa"
  Afham yakara tsuke fuska yana gunguni yace " yanzu ammi saboda amal zaki cemun mutumen banza" cike da hargowa ammi tace "eh nace, maras kunya wadda baya tsoron fushin iyayensa"
   "To shikenan, afham yafada cike da bacij rai yanufi hanyar fita da karfi yaja kofar kamar zai karyata, yafita yana huci yabar dakin"....

Na:- ❤ Rabi'atu sk mash da Mr, Smiles๐Ÿ˜ƒ